A yunkurin ta na tunkarar zaben shugaban kasa a shekarar 2023, jam’iyar PDP ta gudanar da taron gwamnonin ta a nahiyar Turai, domin cimma matsaya a shirye-shiryen fitar da dan takarar shugabanci.
Jaridar THISDAY ta rawaito cewa taron gwamnonin a na yin shine a kasar Spain da Birtaniya, domin ganin jam’iyar ta tsayar da dan takarar ta na shugaban kasa.
Wannan shi ne karo na farko da jam’iyar PDP ta gudanar da taron ta a nahiyar Turai, wanda su ke jiran ranar 30 ga watan Oktoba da kuma 31, domin tsayar da dan takarar shugaban kasa a jam’iyar ta PDP.
A makon da ya gabata ne dai, gwamnonin jam’iyar PDPD su ka gudanar da irin wannan makancin taron a kasar Spain, na cimma matsaya a tsakanin su domin samar da tsayayyen mutum guda da zai kai jam’iyar ta PDP ga gaci a zaben 2023.
Cikin gwamnonin da su ka ziyarci birnin London, sun hadar da Nyesom Wike na jihar Rivers da Seyi Makinde na jihar Oyo da Dr. Okezie Ikpeazu na jihar Abia da kuma Udom Emmanuel na jihar Akwa Ibom.
Yayin taron na jam’iyar PDP, akwai jagoranta, Dr. Iyorchia Ayu wanda ya kasance, domin ganin an warware matsalar samar da mutum guda da zai jagoranci shugabancin jam’iyar.