fidelitybank

2023: Osibanjo ne magajin Buhari – Hafizu Kawu

Date:

Dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Tarauni a jihar Kano, Hafizu Kawu, ya bayyana mataimakin shugaban kasa, Yemi Osibanjo, a matsayin wanda zai gaji shugaban kasa Muhammadu Buhari a zaben 2023.

Da yake jawabi ga manema labarai a Kano ranar Litinin, Kawu, wanda tsohon mai taimaka wa Osibanjo ne, ya ce mataimakin shugaban kasar na da abin da a ke bukata, domin ya gaji Buhari saboda “kwarewa da kwazonsa wajen tafiyar da ayyuka”.

Dan majalisar ya ce, duk da cewa har yanzu mataimakin shugaban kasar bai bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa ba, shi ne ya fi dacewa ya gaji Buhari.

A cewarsa, Osibanjo ya na dagogewa, da kuma iya shugabancin Najeriya a kan duk wani mai neman tsayawa jam’iyyar APC.

Ya ce: “Mataimakin shugaban kasar na da karfin inganta tattalin arzikin kasar ganin cewa shi ne ya tsara duk wani shiri na zuba jari da ya shafi miliyoyin ‘yan Najeriya.

“Na tabbata mataimakin shugaban kasa zai ci gaba daga inda shugaban ya tsaya, domin ya na da tunanin bunkasa Najeriya. Shi ne magajin shugaban kasa. Nijeriya ta na cikin zuciyarsa. Na yi imani sosai a Najeriya. Shi shugaba ne na misali.

“Shi mataimaki ne mai aminci kuma aikinsa a matsayin Mataimakin Shugaban kasa ba a taba ganin irinsa ba. Ko da ya zama shugaban kasa a lokuta da dama, Osibanjo ya taka rawar gani sosai, domin haka ya na da kwarewar zama shugaban kasa a 2023, “inji Kawu.

 

 

ng news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp