fidelitybank

2023: Osibanjo ne magajin Buhari – Hafizu Kawu

Date:

Dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Tarauni a jihar Kano, Hafizu Kawu, ya bayyana mataimakin shugaban kasa, Yemi Osibanjo, a matsayin wanda zai gaji shugaban kasa Muhammadu Buhari a zaben 2023.

Da yake jawabi ga manema labarai a Kano ranar Litinin, Kawu, wanda tsohon mai taimaka wa Osibanjo ne, ya ce mataimakin shugaban kasar na da abin da a ke bukata, domin ya gaji Buhari saboda “kwarewa da kwazonsa wajen tafiyar da ayyuka”.

Dan majalisar ya ce, duk da cewa har yanzu mataimakin shugaban kasar bai bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa ba, shi ne ya fi dacewa ya gaji Buhari.

A cewarsa, Osibanjo ya na dagogewa, da kuma iya shugabancin Najeriya a kan duk wani mai neman tsayawa jam’iyyar APC.

Ya ce: “Mataimakin shugaban kasar na da karfin inganta tattalin arzikin kasar ganin cewa shi ne ya tsara duk wani shiri na zuba jari da ya shafi miliyoyin ‘yan Najeriya.

“Na tabbata mataimakin shugaban kasa zai ci gaba daga inda shugaban ya tsaya, domin ya na da tunanin bunkasa Najeriya. Shi ne magajin shugaban kasa. Nijeriya ta na cikin zuciyarsa. Na yi imani sosai a Najeriya. Shi shugaba ne na misali.

“Shi mataimaki ne mai aminci kuma aikinsa a matsayin Mataimakin Shugaban kasa ba a taba ganin irinsa ba. Ko da ya zama shugaban kasa a lokuta da dama, Osibanjo ya taka rawar gani sosai, domin haka ya na da kwarewar zama shugaban kasa a 2023, “inji Kawu.

 

 

vanguard newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp