Kungiyar Kiristocin Najeriya CAN, ta shawarci shugabannin Najeriya da kada su yi watsi da kokarin da su ke yi na magance dimbin kalubalen da kasar ke fuskanta a yunkurinsu na son kai na samun mukamai a babban zabe mai zuwa na 2023.
A sakonta na sabuwar shekara ga ’yan Najeriya mai dauke da sa hannun shugaban CAN, Rabaran Samson Ayokunle, kungiyar ta bukaci kowa ya yi amfani da damar shiga sabuwar shekara, domin yin azumi da addu’o’i na rokon Allah ya kubutar da Nijeriya daga wadanda su ke da niyyar ruguza ta.
Kungiyar ta CAN ta koka da yadda ayyukan ‘yan fashi da ‘yan ta’adda, masu garkuwa da mutane da sauran abubuwan rashin gaskiya su ka sanya akasarin sassan Najeriya cikin rashin tsaro.
Ya ce,”Masu aikata laifuka sun mamaye kasar, sun mamaye al’ummomi, kasuwanni, coci-coci da makarantu suna kashewa, lalata da lalata dukiyoyi ba tare da tsangwama”. Inji Rabaran.
Kungiyar ta CAN ta kuma koka kan yadda a yanzu ya zama babban abin da ‘yan siyasa ke mayar da hankali a kai shi ne zaben 2023.
“2021 shekara daya ta yi yawa a sakamakon hanyoyi da dabi’u da wadannan miyagu ke gudanar da ayyukansu ba tare da hukunta su ba, kamar ba kasar nan ba ce da mu ka kasance a wadannan shekarun.
“Allah ne kadai zai iya tabbatar da zaben 2023 mai zuwa. Allah ne kawai a hanyarsa wanda zai iya koya wa shugabanninmu matakin da ya dace. Allah ne kadai zai iya aiko mana da taimako daga sama. Saboda halin da mu ke ciki, tuni wasu gwamnonin ke ta kiraye-kirayen a kare kansu da kuma ayyana dokar ta-baci! Wannan ba irinsa ba ne.
“Ina kira ga daukacin mabiya darikar mu da shuwagabannin cocin mu da su yi amfani da damar shirin azumi da addu’o’in sabuwar shekara na coci-cocin mu, domin kubutar da Nijeriya daga wadanda su ke da niyyar ruguza ta ta hanyar yin addu’a da gangan, domin neman rahamar Allah a kan halin da mu ke ciki. Gama Ubangiji Allah mu Allah ne mai jinƙai. Ba zai bar mu ba ko ya bar wadannan miyagu marasa zuciya su halaka mu,” in ji CAN.