fidelitybank

2023: Babu hannu na a fastocina da suka mamaye kasar nan – Orji Uzor Kalu

Date:

Bulaliyar majalisar dattawa, Sanat Orji Uzor Kalu, ya sha musanta hannu a cikin fastocin da suka rika fitowa a kusan dukkanin jihohin tarayyar kasar nan, da nufin tallata burinsa na neman tikitin takarar shugaban kasa na gaba

Kalu ya bayyana hakan ne a cikin wani sako da mai taimaka masa a bangaren Arewa, Aminu Shehu Uba Sharada, ya aikewa manema labarai.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, Sanata Orji Uzor Kalu ya na son komawa majalisar dattawa a 2023 a matsayinsa na wakilin gundumar Abia ta Arewa.

Duk da rashin amincewa da tawagarsa ta yi, an sake bayyana fastocin tsohon gwamnan jihar Abia, Orji Uzor Kalu a matsayin dan takarar shugaban kasa a wasu manyan biranen kasar nan.

Fastocin sun mamaye fitattun wurare da suka hada da Katsina da Gasau da Owerri da Enugu da Kano da Maiduguri da Lagos da dai sauransu.

Fastocin da a ka gani a karshen mako su na dauke da sakon, cewa ‘Yan Najeriya na bukatar ka ORrji Uzor Kalu, matasan Arewa 19 sun dawo tafiyar ka OUK.

Ambaliyar fastocin a manyan biranen kasar na zuwa ne kwanaki kadan, bayan wata kungiyar da a ka fi sa ni da Kudu maso Gabas ta Orji Uzor Kalu ta bayyana cewa suna kaddamar da ofisoshin su a jihohi 34 na tarayyar kasa nan.

Kodinetan kungiyar, Fasto Ejike Nwachukwu, ya bayyana cewa. wanda a ka sa ni a Enugu ranar Alhamis, yayin da ya ke kaddamar da Daraktoci na Jihar Kudu-maso-Gabas, inda ya bayyana cewa, kungiyar ta samu ofisoshi a cikin jihohi kusan 34 na tarayya.

 

latest news in nigeria today 2022 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar Æ´an Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaÉ“e shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Æ´an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation HaÉ—in-Kai sun ce sun kashe Æ´an...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aÆ™alla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp