Bulaliyar majalisar dattawa, Sanat Orji Uzor Kalu, ya sha musanta hannu a cikin fastocin da suka rika fitowa a kusan dukkanin jihohin tarayyar kasar nan, da nufin tallata burinsa na neman tikitin takarar shugaban kasa na gaba
Kalu ya bayyana hakan ne a cikin wani sako da mai taimaka masa a bangaren Arewa, Aminu Shehu Uba Sharada, ya aikewa manema labarai.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, Sanata Orji Uzor Kalu ya na son komawa majalisar dattawa a 2023 a matsayinsa na wakilin gundumar Abia ta Arewa.
Duk da rashin amincewa da tawagarsa ta yi, an sake bayyana fastocin tsohon gwamnan jihar Abia, Orji Uzor Kalu a matsayin dan takarar shugaban kasa a wasu manyan biranen kasar nan.
Fastocin sun mamaye fitattun wurare da suka hada da Katsina da Gasau da Owerri da Enugu da Kano da Maiduguri da Lagos da dai sauransu.
Fastocin da a ka gani a karshen mako su na dauke da sakon, cewa ‘Yan Najeriya na bukatar ka ORrji Uzor Kalu, matasan Arewa 19 sun dawo tafiyar ka OUK.
Ambaliyar fastocin a manyan biranen kasar na zuwa ne kwanaki kadan, bayan wata kungiyar da a ka fi sa ni da Kudu maso Gabas ta Orji Uzor Kalu ta bayyana cewa suna kaddamar da ofisoshin su a jihohi 34 na tarayyar kasa nan.
Kodinetan kungiyar, Fasto Ejike Nwachukwu, ya bayyana cewa. wanda a ka sa ni a Enugu ranar Alhamis, yayin da ya ke kaddamar da Daraktoci na Jihar Kudu-maso-Gabas, inda ya bayyana cewa, kungiyar ta samu ofisoshi a cikin jihohi kusan 34 na tarayya.