fidelitybank

2022: Siyasar zage-zage za ta iya kawo cikas a Najeriya – Orji Kalu

Date:

Tsohon gwamnan jihar Abia kuma bulaliyar majalisar dattawa, Dr. Orji Kalu ya bukaci ‘yan Najeriya da su jajirce tare da kishin kasa da kuma nuna kyakkyawan fata, domin shiga sabuwar shekara a sa’a.

Kalu yayin da ya ke jinjina wa ‘yan kasar kan yadda su ke ci gaba da marawa shugaban kasa Muhammadu Buhari baya, ya gargadi ‘yan siyasa da su guji yin siyasar zage-zage da za su iya kawo cikas ga kasar nan.

Tsohon Gwamnan ya jaddada cewa, dole ne shugabanni a kowane mataki na gwamnati su tabbatar da jin dadin al’umma, shi ne babban abin da zai sa a gaba a manufar su, ya kuma kara da cewa, dole ne gwamnati da masu mulki su taka rawar da za ta dace wajen gina kasa ta Najeriya mai ci gaba, hadin kai da mai dorewa.

Kalu, wanda ya bayyana haka a gidansa na Igbere, a lokacin rabon kyaututtukan karshen shekara ga al’ummar mazabarsa a wani bangare na ayyukansa na karshen shekara, ya yi kira ga ‘yan Najeriya masu kishin kasa da su rungumi ayyukan jin kai.

Ya ce, “Sabuwar shekara, ya zama wajibi mu yi la’akari da nasarorin da mu ka samu da kalubalen da mu ka samu a daidai ku da kasa baki daya”.

“Babu shakka, 2021 shekara ce ta tunani da kuma biki.

“Domin kasar nan ta kai wani matsayi na kishi, dole ne mu guji ayyukan da za su raba kasar nan.

“Lokaci ya yi da ‘yan Nijeriya ba tare da la’akari da bambance-bambancen siyasa, kabilanci da addini ba, ya kamata su wanzar da zaman lafiya da juna a wani yunkuri na gina al’umma mai adalci.

“Ba wata kasa da za ta ci gaba a cikin yanayin rashin jituwa.

“Dole ne a yi amfani da bambancin al’adu da kabilanci da addini a Najeriya domin ci gaban kasar.

“Bai kamata mu bar ra’ayin siyasa ko addini ya mayar da Najeriya baya ba.

“Bari mu sanya mutane cikin gwamnati cikin zarge-zarge masu ma’ana da suka saba wa kalaman kyama da yakin neman zabe.

“A cikin sabuwar shekara, dole ne mu yi kyawawan halaye a cikin ayyukan mu na yau da kullun, domin tabbatar da zaman lafiya da hadin kai.” Inji Kalu.

Tsohon Gwamnan ya yi wa ‘yan Najeriya fatan nasara a sabuwar shekara.

national news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...
X whatsapp