fidelitybank

Ƴan sanda sun kama mutum 4 a zanga-zangar masu kiwon zuma a ƙasar Chile

Date:

Ƴan Sanda a ƙasar Chile sun kama mutum huɗu da ga cikin masu kiwon zuma da bayan da su ka yi zanga-zanga a fadar shugaban ƙasa a Santiago.
Kamfanin Daillancin Labarai na Reuters ya rawaito cewa masu kiwon zumar, a ƙarƙashin ƙungiyar su, sun girke kwangin zuma kusan 60 mai ɗauke da ƙudan zuma kimanin dubu 10 a ciki.
Bayan da su ka fara zanga-zangar ne sai ƙudan zuman su ka fara tasowa, inda su kai kan me-uwa-da-wabi su ka riƙa gasawa ƴan sandan cizo.
Rahotanni dai sun baiyana cewa ƴan sanda 7 ne su ka sha cizon ƙudan zumar, inda saura kuma su ka ranta a na kare.
Farin da ƙasar ta shiga ne tun shekarar 2010 ya shafi noman zuma a ƙasar, sakamakon fulawowi da tsirrai da ciyawu ba sa fitowa saboda rashin ruwa inda kuma su ne abincin da zuma ke ci ta rayu.
Ƴan ƙungiyar sun koka cewa farin na sanyawa kudan zuma na mutuwa kuma yawan su na raguwa, in da su ka nuna cewa mutuwar ƙudan zuma ɗaya, illa ce ga duniya baki daya.
Masu zanga-zangar, waɗanda su ka rufe wasu manyan titunan birnin sun yi kira ga gwamnati da ta farfaɗo da noman zuma domin tattalin arzikin manoman ya dawo.
Sun kuma nemi su gana da shugaban ƙasar Chile, Sebastian Pinera.
A halin yanzu dai, tuni ƴan sanda su ka cafke mutane huɗu a cikin masu zanga-zangar.

www.legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp