Wasu gungun ƴan daba, ɗauke da muggan makamai ne su kai hari kan ofishin kamfe na Sanata Barau Jabril a Jihar Kano.
Jaridar PlatinumPost ta rawaito cewa ɗaruruwan ƴan daban sun dira a ofishin da ke Titin Maiduguri, a birnin Kano, inda su ka faffasa kujeru da tebura, gami da allukan da ke ɗauke da fastocin ƴan takara, sannan su ka ƙona wani sashe na ofishin.
A jiya Laraba ne dai gwamnatin Kano ta garƙame ofishin lauyan da ya tsayawa ɓangaren Shekarau, Nureini Jimoh, su ka samu nasara a shari’ar da kotu ta rushe shugabannin jam’iya na Kano, ƙarƙashin Abdullahi Abbas.
Kakakin ƴan sanda na Jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa bai samu damar amsa wayar wakilin mu ba.
Amma daga bisani ya aiko da gajeren saƙo, in da ya ce yana wata ganawa ne.