fidelitybank

Ɗalibai miliyan 1,205,888 za su zana jarabawa – NECO

Date:

Hukumar shirya jarabawar ta kasa (NECO), ta sanya adadin wadanda suka yi rijistar zana jarrabawar kammala sakandare na shekarar 2023 da ke gudana a kan mutane miliyan daya da dubu dari biyu da biyar da dari takwas da tamanin da takwas, (1,205,888).

Shugaban Hukumar NECO, Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi ne ya bayyana hakan a Jos Jihar Filato ranar Juma’a, yayin da yake sa ido kan yadda ake gudanar da jarabawar a wasu makarantu.

Farfesa Wushishi wanda ya yi magana ta hannun sashin yada labarai da hulda da jama’a na HOD Azeez Sani, ya bayyana cewa a cikin wannan adadi mutane 601,074 maza ne yayin da 584,814 mata ne.

Ya nuna jin dadinsa da yadda aka gudanar da zaben 2023 na SSCE gaba daya bisa rahotannin da aka samu daga sassan kasar nan.

Magatakardar ya kuma lura cewa 2023 SSCE da za a kammala mako mai zuwa ita ce mafi kyawun tsari a cikin ‘yan shekarun nan.

Farfesa Wushishi ya bayyana cewa, an dauki matakai daban-daban na duba kura-kuran jarabawar, inda ya kara da cewa matakan sun fara samun sakamako mai kyau.

Magatakardar da ta sa ido a jarabawar a makarantar Soja ta Airforce; King and Queens Academy da Emmanuel International College duk a Jos, sun bayyana gamsuwarsu da yadda aka gudanar da jarabawar a makarantun da suka ziyarta.

Tun da farko Farfesa Wushishi ya sanya ido kan yadda 2023 SSCE ke gudana a jihohin Kebbi, Sokoto, Zamfara, Katsina, Kano, Jigawa da Bauchi.

leadership newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp