fidelitybank

Ƴan sanda sun kama mutum 4 a zanga-zangar masu kiwon zuma a ƙasar Chile

Date:

Ƴan Sanda a ƙasar Chile sun kama mutum huɗu da ga cikin masu kiwon zuma da bayan da su ka yi zanga-zanga a fadar shugaban ƙasa a Santiago.
Kamfanin Daillancin Labarai na Reuters ya rawaito cewa masu kiwon zumar, a ƙarƙashin ƙungiyar su, sun girke kwangin zuma kusan 60 mai ɗauke da ƙudan zuma kimanin dubu 10 a ciki.
Bayan da su ka fara zanga-zangar ne sai ƙudan zuman su ka fara tasowa, inda su kai kan me-uwa-da-wabi su ka riƙa gasawa ƴan sandan cizo.
Rahotanni dai sun baiyana cewa ƴan sanda 7 ne su ka sha cizon ƙudan zumar, inda saura kuma su ka ranta a na kare.
Farin da ƙasar ta shiga ne tun shekarar 2010 ya shafi noman zuma a ƙasar, sakamakon fulawowi da tsirrai da ciyawu ba sa fitowa saboda rashin ruwa inda kuma su ne abincin da zuma ke ci ta rayu.
Ƴan ƙungiyar sun koka cewa farin na sanyawa kudan zuma na mutuwa kuma yawan su na raguwa, in da su ka nuna cewa mutuwar ƙudan zuma ɗaya, illa ce ga duniya baki daya.
Masu zanga-zangar, waɗanda su ka rufe wasu manyan titunan birnin sun yi kira ga gwamnati da ta farfaɗo da noman zuma domin tattalin arzikin manoman ya dawo.
Sun kuma nemi su gana da shugaban ƙasar Chile, Sebastian Pinera.
A halin yanzu dai, tuni ƴan sanda su ka cafke mutane huɗu a cikin masu zanga-zangar.

legit nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp