fidelitybank

Ƴan bindiga sun yi awon gaba da mutane lokacin da suke sallar Magariba

Date:

Akalla mutane 14 ne aka yi garkuwa da su a lokacin da wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne suka kai hari a wani masallaci da ke karamar hukumar Giwa a jihar Kaduna.

Rahotonni sun ce, daya daga cikin masu ibadar, Alhaji Buhari Nadama, wanda ya ce da kyar ya tsere, ya bayyana cewa, sun ji karar harbe-harbe a lokacin da suke sallar magariba.

Ya ce, bayan mintuna kadan, sai suka ga wasu mutane da suka rufe fuska, wadanda ke dauke da makamai.

A cewarsa, ‘yan bindigar sun kuma tafi da wasu shanu daga wata unguwar da ke kusa da su, Tudun Amada.

Har ila yau, wani shugaban al’ummar yankin, Alhaji Dauda Mustapha ya bayyana cewa, yayin da wasu ‘yan ta’addan ke gudanar da ayyukansu a cikin masallacin, wasu kuma sun binciki gidaje da dama, inda suka dauko mata.

Sai dai wani mazaunin garin ya shaidawa kafar yada labarai cewa, an sako hudu daga cikin wadanda aka sace a daren Juma’a.

A halin yanzu, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan Kaduna, ASP Mohammed Jalige bai tabbatar da faruwar lamarin ba.

nigerianewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp