Ƴan bindiga sun sace ɗalibai mata biyu na jami’ar tarayya da ke Gusau a jihar Zamfara.
Rahotonni sun ce ‘yan fashin ɗauke da muggan makamai, sun sace ɗalibai mata guda biyu a ɗakunan kwanansu da ke wajen makarantar.
A wata sanarwa da rundunar ‘yan sandan jihar ta fitar, ta ambato kwamishinan ‘yan sandan jihar CP Kolo Yusuf na tabbatar wa da dangin ɗaliban da kuma hukumar makarantar cewa rundunar na ƙoƙari wajen kuɓutar da ɗaliban.
Sanarwar ta ce, rundunar ‘yan sandan ta samu labarin sace ɗaliban a ɗakunan kwanansu da ke a wajen makarantar.
Tun bayan samun labarin sace ɗaliban ne, rundunar ‘yan sandan ta ce ta tura jami’anta zuwa wajen da lamarin ya faru, to sai dai kafin zuwan jami’an tsaron ‘yan fashin sun tsere da ɗaliban, kamar yadda sanarwar ta bayyana.
Haka kuma sanarwar ta ce kwamishinan ‘yan sandan ya tura ƙarin jami’an tsaro domin kuɓutar da ɗaliban, tare da kama ‘yan fashin domin gurfanar da su a gaban shari’a.
Daga ƙarshe kwamishinan ‘yan sandan jihar ya yi kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa jami’an tsaron haɗin kai domin samun nasarar kuɓutar da ɗaliban