fidelitybank

‘Ƴan APC za su karɓi kuɗin Tinubu kuma su ƙi zaɓar sa a 2023’

Date:

Babban Fasto na Cocin Divine Mercy, Olatobiloba Peters ya yi hasashen cewa ƴan jam’iya mai mulki ta APC za su ci kuɗin Bola Ahmed Tinubu ne kawai su kuma ko zabar sa.
Ya kuma gargaɗi Tinubun, mai neman tsayawa takarar shugaban ƙasa a 2023 da kada ya ci gaba da burinsa na zama shugaban ƙasa.
Fasto Peters ya ce ƴan jam’iyyar  APC, za su karɓi kuɗin Tinubu kawai kuma su ƙi kaɗa masa ƙuri’a.
Da yake zantawa da DAILY POST, limamin ya ce Ubangiji ne ya nuna masa cewa ‘yan APC za su yi amfani da kudin Tinubu su cicciɓa mataimakin shugaban kasa, Osinbajo ya zama shugaban kasa.
Tinubu, wanda ya sanar da shugaban kasa Muhammadu Buhari aniyarsa ta tsayawa takarar shugabancin kasar a 2023, ya ce matakin wani buri ne a gare shi tsawon rayuwarsa.
Jagoran jam’iyyar APC na Ƙasa ya ce yana ci gaba da tuntuɓar masu ruwa da tsaki a kan matakin da ya ɗauka na maye gurbin Buhari a 2023.
Sai dai Fasto Peters ya ce Ubangiji ya halicci Tinubu ne domin ya kafa sarakuna ba wai shi ya zama ba.
Limamin ya bukaci tsohon gwamnan jihar Legas ɗin da kada ya barnatar da kudinsa a kan kudirinsa na shugaban kasa.
Sai dai ya yi gargadin cewa ‘yan Najeriya za su yi nadama idan har Tinubu ya tilasta wa kan sa mulki ta hanyar magudi.

assu update

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buƙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...
X whatsapp