fidelitybank

Ƴan Adaidaita-sahu sun fara  yajin aiki a Kano

Date:

 

 

Direbobin babur mai ƙafa uku, wanda a ka fi sani da adaidaita-sahu a Jihar Kano sun tsunduma yajin aikin gargaɗi na mako ɗaya da ga yau Litinin.

Tun a ranar 30 ga watan Disambar da ya gabata ne ƴan adaidaita-sahun su ka yi barazanar tsunduma yajin aiki.

Matakin na su ya biyo bayan ci gaba da gudanar da zanga-zangar lumana da suke yi bisa umarnin sauya lambar babur ɗin da hukumar KAROTA ta ba su inda su ka yi zanga-zanga ta lumana a jihar.

Zanga-zangar dai ta biyo bayan yadda hukumar KAROTA ta ce sai sun biya kudi Naira 8,000 domin sabunta lambar ta su.

Sun kuma koka kan yadda KAROTA ke karɓar kuɗaɗen haraji barkatai a hannun su, musamman ma naira 100 da su ke biya kullum.

A cewar su, ba biyan naira 100 ɗin ne ke damun su ba, wacce su ke biya ta ranar lahadi, duk da cewa jami’an karɓar harajin ba sa fita aiki a ranar, amma a washegari Litinin sai a ce sai su biya har da ta ranar Lahadin.

“Kuma fa har yanzu ba a bamu na’urar nan ta ganin inda mai adaidaita-sahu ya ke ba, duk da cewa mun biya kuɗin tun sama da shekara ɗaya.

“Kullum sai an karbi kuɗaɗe a hannun mu kuma ba ma ganin amfanin kuɗin da mu ke biya,” in ji wani direban adaidaita-sahu.

Da ga ƙarshe, matuƙa baburan sun baiyana cewa da ga lokacin da hukumar KAROTA ta fara kamasu, su ma za su tafi yajin aiki.

Daily Nigerian Hausa ta gano cewa tun a jiya dai matuƙa baburan su ka raba sanarwar tafiya yajin aikin, duk da cewa takardar sanarwar ba ta ɗauke da sa hannun kowa, inda su ka umarci matuƙa adaidaita-sahu da su zauna a gida, su ka kuma yi barazanar kama babur ɗin masu kunnen ƙashi a cikin su.

Sai dai kuma tun a jiyan, jaridar nan ta gano cewa da yawa da ga matuƙa baburan adaidaita-sahun sun fara saka ganye a jikin baburan na su, inda hakan ke nufin shirye-shiryen tsunduma yakin aiki a yau.

A tuna cewa tun a farko-farkon shekarar da mu ke bankwana da ita ne matuƙa baburan adaidaita-sahu su ka tafi yajin aiki sakamakon harajin naira 100 da a ka sanya musu a kullum, inda hakan ya kawo naƙasu a kan al’amuran yau da kullum a jihar.

thisday newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...
X whatsapp