Dan kwallon Najeriya Abubakar Lawal ya rasu a kasar Uganda.
A cewar rahoton, Lawal ya fado ne daga barandar kantin sayar da kayayyaki da ke birnin Kampala, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwarsa.
‘Yan sandan Uganda sun ce a yau Litinin suna gudanar da bincike kan mutuwar dan wasan.
Lawal, mai shekara 29, dan wasan gaba, ya taka leda a kulob din firimiya na gida, Vipers.
Sanarwar da ‘yan sandan ta fitar ta ce dan kwallon ya fado ne daga hawa na uku na tashar Voicemall Shopping Arcade da safiyar ranar Litinin.
An ce dan Najeriyar ya ziyarci wani abokinsa dan kasar Tanzaniya da ke zama a daya daga cikin gidajen zama da ke wani bangare na kasuwar.
Channels ta ruwaito cewa wata kawarta ta shaida wa ‘yan sanda cewa ta bar shi shi kadai jim kadan kafin faduwar.
“Hukumomi suna dawo da hotunan CCTV tare da gudanar da cikakken bincike don gano ainihin yanayin da ya faru,” in ji ‘yan sanda.
Kungiyar wasanni ta Vipers a cikin wata sanarwa da ta fitar ta ce: “Muna matukar bakin cikin sanar da rasuwar abin kaunarmu, Abubakar Lawal, wanda ya bar mu da safiyar yau.
“Tunaninmu da addu’o’inmu suna tare da dangin Lawal, magoya bayan kulob, abokai da kuma masoya a wannan mawuyacin lokaci,” in ji ta.
Lawal ya koma kungiyar wasanni ta Vipers a watan Yulin 2022 daga AS Kigali a kasar Rwanda.