fidelitybank

Ɗan takarar mu Obi ake hari ba jam’iyyar mu ba – LP

Date:

Dr Tanko Yunusa, mai magana da yawun majalisar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, ya ce, rikicin da ya dabaibaye shugabannin jam’iyyar ba wai kan shugaban jam’iyyar na kasa Julius Abure ne ba, sai dai an kai shi ne kan Peter Obi.

Rikicin da ya biyo bayan zaben jam’iyyar Labour ya dauki wani salo a ranar Alhamis bayan da rundunar ‘yan sandan Najeriya ta rufe sakatariyarta kan rikicin shugabanci a tsakanin shugabanninta.

Karanta Wannan: Zaɓaɓɓen Gwamnan Kano ya gargaɗi shugabannin ƙananan hukumomi

Yunusa ya bayyana haka ne a ranar Laraba yayin wata hira da gidan Talabijin na Channels; ya ce rudanin da ke cikin jam’iyyar LP an shirya shi ne domin ya bata dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Peter Obi, wanda ke gaban kotu, domin kalubalantar nasarar Bola Ahmed Tinubu a zaben da aka yi a ranar 25 ga watan Fabrairu.

“Muna kan fafutukar ganin an ceto Najeriya karkashin jagorancin Peter Obi; A yanzu haka ana tsoma baki tare da yi mana magudi a cikin jam’iyyar, domin kalubalantar shugabancin jam’iyyar da ke kan gaba wajen wannan gwagwarmaya, sannan a bar gaskiya ga wasu abubuwa. Ba ina nuni da cewa ba su da wata takarda da za ta tabbatar da Julius Abure; wannan ya kamata a yi a cikin jam’iyyar.

“Na bayyana a fili cewa abin da ake so ya wuce shugaban jam’iyyar; ya saba wa dan takarar shugaban kasa, Peter Obi,” inji shi.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

QPC ta nemi INEC ta soke zaɓen Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Rudunar ƴansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum...

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...

Farashin kayan abinci na rugu-rugu a Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin...

Kotun Kano ta ce a kamo mata Dagacin Tamburawa

Kotun Shari’ar Musulunci da ke shelkwatar Hisbah a Kano,...

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar...

A na cigaba da gudanar da zaben cike gurbi harda Kano

Kano na ɗaya daga cikin jhihohin da ake kaɗa...

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...
X whatsapp