fidelitybank

Ɗan Sandan da mawaki Kuti ya mara ya samu ƙarin girma

Date:

Mohammed Aminu, dan sandan da mawakin Afrobeat Seun Kuti ya mara ya samu karin girma.

A cikin watan Mayu, an ga Kuti a cikin wani faifan bidiyo na bidiyo yana cin zarafin dan sandan, wanda duk da tsokanarsa bai yi komai ba.

Daga baya an tsare Kuti aka gurfanar da shi a gaban kuliya bisa laifin cin zarafi, inda ya ce bai aikata laifin ba kuma an bayar da belinsa.

A wata sanarwa da hukumar ‘yan sanda ta fitar a ranar Alhamis ta ce an karawa jami’in karin girma zuwa mukamin mataimakin Sufeton ‘yan sanda (ASP).

A wata sanarwa da mai magana da yawun PSC, Ikechukwu Ani ya fitar, ya ce Aminu, duk da harin, ya nuna kwarewa sosai.

“Sufeto Mohammed Aminu, wanda ya yi ta yawo a kafafen sada zumunta inda aka gan shi yana cin zarafi da wani Seun Kuti, shi ma an kara masa girma zuwa ASP I,” in ji Ani.

A zamanta na 21 da hukumar ta ke ci gaba da yi, ta amince da nadin mataimakin Sufeto Janar (DIG) guda biyu tare da karawa jami’in hulda da jama’a na rundunar, CSP Muyiwa Adejobi karin girma zuwa mukamin mataimakin kwamishinan ‘yan sanda (ACP).

Ani ya bayyana cewa 9,016 ba a tabbatar da mataimakan Sufurtandan ‘yan sanda (ASP) ba, an kuma amince da karin girma ga sufeto 14,052 zuwa mataimakan Sufiritandandan ‘yan sanda (ba a tabbatar da su ba).

“An kara wa wani Sufeto Habila Bulus karin girma zuwa ASP II saboda jajircewarsa,” in ji Ani.

An bayyana cewa, Olalaye Falaye, tsohon kwamishinan ‘yan sanda na jihar Ebonyi ya samu karin girma zuwa mukamin mataimakin sufeto Janar (AIG).

breaking news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp