Geng Quanrong, mutumin da ake zargi da kashe Ummu Buhari (Ummita), za a ba shi abincin kasar Sin.
Hukumar kula da gyaran hali ta Najeriya (NCS) ta tabbatar da hakan yayin da ake ci gaba da shari’ar sa a Kano.
Mai magana da yawun gidan gyaran hali na Kano, Musbahu Kofar-Nassarawa ya ce, ba a sa ran Quanrong ya ci ‘gabza’, abincin fursunoni.
Jami’in hulda da jama’a ya ce dokar ta tanadi cewa bakon da ke tsare a gidan yarin Najeriya ya kamata a ciyar da shi da abincinsa.
Kofar-Nasarawa ya kara da cewa dokar ta ba wa irin wadannan fursunonin damar tuntubar ofishin jakadancin kasarsu ko ‘yan uwansu don neman taimako.
“Mutane suna tambayar wane irin abinci ne wanda ake zargin zai ci.
“Za a ba shi abinci na kasar Sin, abin da doka ta tanada kenan,” Daily Nigerian ta ruwaito yana cewa.
An gurfanar da Quanrong a gaban kotu a ranar Laraba amma ba a amsa rokonsa ba saboda rashin hurumi.
Alkalin kotun Mai shari’a Hanif Sanusi ya dage sauraron karar kisan zuwa ranar 13 ga watan Oktoba domin baiwa jihar damar yin shirye-shiryen da suka dace.