fidelitybank

Ɗaliban Sakandire sun zane Malamin da ya hana su satar jarabawa

Date:

Wasu gungun daliban makarantar sakandire su 10 a jihar Ogun, sun kai wa wani malaminsu hari, wanda ya hana su yin magudi a lokacin jarrabawar zango na uku da ya gabata.

Daliban makarantar Isanbi Comprehensive High School dake Ilisan-Remo a karamar hukumar Ikenne a jihar Ogun, sun yi zane malamin Kolawole Shonuga a ranar Talata.

An tattaro cewa Shonuga a lokacin da yake zagaya jarabawar gama-gari na daliban aji SS 1, ya kama daya daga cikin yaran mai suna Ashimi Adebanjo mai shekaru 18 yana yin magudi, kuma ya kwace takardarsa.

Wani ganau ya bayyana cewa bayan an kammala karatun sa’o’i ne daliban suka taru a wani wuri, inda suka yi wa malamin duka a kofar makarantar.

An tattaro cewa, daya daga cikin yaran mai suna Kazeem Adelaja ya buga sanda a kan Shonuga yayin da wasu ke dukansa.

A halin da ake ciki, jami’an ‘yan sanda daga reshen Remo sun kama wasu adadi mai yawa na wadanda ake zargin.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, Omotola Odutola, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce, Shonuga ya bayar da rahoton a ofishin ‘yan sanda na Remo, yayin da ya tabbatar da kama mutane 10 da ake zargi.

Shugaban kungiyar malaman makarantun sakandire (ASUSS) na jihar, Felix Agbesanwa ya fusata kan lamarin, inda ya jaddada cewa “duk dalibin da ya daga hannu a kan malaminsa to ya fuskanci fushin doka.”

Shi ma mai baiwa gwamna shawara kan harkokin ilimi, kimiya da fasaha Farfesa Abayomi Arigbabu, ya yi Allah wadai da abin da daliban suka yi tare da shan alwashin cewa, gwamnatin jihar ba za ta amince da ayyukan rashin da’a da dalibai ke yi a fadin jihar ba.

news today in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp