fidelitybank

Ɗalibi ya rataye kansa da saboda Jarabawar makaranta

Date:

Wani dalibi ɗan shekara 17 a makarantar Offa Grammar dake karamar hukumar Offa a jihar Kwara mai suna Adegoke Adeyemi ya kashe kansa sakamakon rashin cin jarabawar karin aji daga SS1 zuwa SS2.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Kwara, Okasanmi Ajayi, a wata sanarwa da ya fitar a Ilorin a daren ranar Laraba, ya ce, an bukaci ɗalibin da ya sake karatun ajin, amma ya ji kunya kuma ya kashe kansa.

An yi imanin cewa, ya rataye kansa ne sakamakon gaza cin jarabawar ci gaba da daga SS1 zuwa SS 2, wanda hakan ya sa ya zama dole ya rataye kansa.

Tawagar ‘yan sanda daga hedikwatar ‘yan sanda ta ofishin Offa, da misalin karfe 15.34 ne suka kwashe gawar dalibin daga wata bishiya a bayan Otal din Ariya Garden, Offa. In ji Daily Nigerian.

An kai gawar zuwa babban asibitin Offa domin a tantance gawarwakin, yayin da aka fara bincike kan lamarin.

A halin da ake ciki kuma, rundunar ‘yan sanda, ta ce rundunar ta samu nasarar cafke wani fitaccen dan kungiyar asiri a cikin jerin sunayen da ake nema ruwa a jallo na kungiyar masu yaki da ‘yan daba a ACE Supermarket, Unity Road, a lokacin da ta kama dan ta’addan mai suna Monday Ojoagbu.

Kakakin ya ce, ‘yan sanda sun kama shugaban ne a babban kanti inda aka gano su da misalin karfe 6 na yammacin ranar Talata.

Ya kara da cewa: “A kokarin kamo wanda ake zargin, tare da kaucewa yin barna a cikin aikin kama shi, abu ne mai wahala a lokaci guda a kama sauran ‘yan kungiyarsa da suka tsere ta hanyar amfani da kwastomomin babban kanti a matsayin garkuwa.

“Ana ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin. An samu nasarar kwato bindiga guda daya na cikin gida da harsashi masu rai guda biyu daga hannun wanda ake zargin.”

the nation newspaper 
today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp