fidelitybank

Ɓarawo ya rasu ya na ƙoƙarin yin sata a ƙarƙashin mota

Date:

 

 

An tsinci gawar wani mutum da a ke zargin ɓarawo ne a ƙarƙashin wata mota a Ago Egun, bodar Idiroko da ke Jihar Ogun.

Jaridar Tribune ta rawaito cewa a na zargin ɓarawon ya yi yunƙurin kwance wasu muhimman abubuwa a jikin motar, amma sai jak ɗin ɗaga mota da ya yi amfani da shi wajen ɗaga motar ya goce bayan ya riga ya shiga ƙarƙashin ta, inda motar ta faɗo masa.

Soji Gonzalo, Kwamandan rundunar bijilante ta jihar, ya baiyana cewa su na cikin sintiri ne sai su ka ga gawar mutum a ƙarƙashin wata tsohuwar mota a wani garejin gyaran mota.

Ya ƙara da cewa sun gano gawar mutumin ne da misalin ƙarfe 6 na yamma a Ago Egun ranar Alhamis.

Gonazlo ya baiyana cewa binciken su na farko ya nuna cewa motar ta daɗe a garejin wanda sama da shekara biyu ba amfani da shi kuma duk yi kurin samun wanda ya ke da filin garejin ya ci tura.

“A yanzu dai mun ɗauke gawar da kuma jak da mu ka samu mai launin ja da kuma almakashi da sauran sifanu za mu kai wa ofishin ƴan sanda na Idiroko domin faɗaɗa bincike,” in ji Gonzalo.

 

dailysun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp