Rundunar ƴansanda a Abuja, babban birnin Najeriya ta ce ta kama wasu mutane 15 da ake zargi da hannu wajen fasa rumbun adana abinci a birnin.
Wasu matasa ne suka fasa rumbun ajiya kayan abincin na hukumar kai gajin gaggagawa ta ƙasar, a yankin Gwagwa.
Bayanai sun nuna cewa matasa sun yi wa rumbun ƙarƙaf, ko da yake ƴansandan sun ce sun kwata buhu 26 na masarar da ake zargin an kwashe.
Ƴansandan sun kuma ce sun kwato babura biyar daga mtanen da aka cafke.
A ƙarshen mako ne wasu matasa suka daka wa wata babbar mota mai ɗauke da taliya wawa, kuma har yanzu babu rahoton kama wani.
matalar fasa rumbun abinci ko motocin da ke ɗauke da kayn abinci, batu ne da ke c gaba da faruwa a sassan ƙasar daban-daban.
Miliyoyin ƴanƙasar ne ke rayuwa cikin ƙangin talauci, lamarin da ya jefa da dama cikin halin yunwa da ƙarancin abinci.
Tun bayan janye tallafin mai a watn Mayun da ya gabata ne, farashin kayyayaki, musamman na abinci suka yi tashin gwauro zabi a ƙasar.