fidelitybank

Ƴansanda sun kama Mutane 1,254 da suka aikata laifi cikin shekara guda a Jigawa

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta kama wasu mutane 1,254 da ake zargi da aikata laifuka da suka hada da garkuwa da mutane, fashi da makami, sata, barna da sauransu.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar CP. AT. Abdullahi ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai nasarorin da rundunar ta samu a shekarar 2024.

A cewarsa, an kama mutane 1,254 bisa manyan laifuka daga ranar 20 ga Nuwamba, 2023 zuwa yau.

“Mutane tamanin da takwas (88) da ake zargi da yin fashi da makami, da masu garkuwa da mutane goma sha tara (19), wadanda ake zargi da aikata laifin fyade dari da ashirin (120) da kuma dari da hamsin da takwas (158) da ake zargin sun aikata laifin kisan kai.

“Sauran sun hada da, mutane dari takwas da sittin da tara (869) da ake zargi da aikata wasu laifuka kamar: Barna, Satar Shanu, Satar Dabbobi, Satar Muggan Kwayoyi, Satar Babura, Satar Motoci da Zamba.

“An kwato bindigogi goma sha bakwai (17), da suka hada da guda uku (3) AK-47, Bidistol daya (1), Bindigogin Dane guda goma (10), bindigu na gida guda uku (3) da kuma harsasai guda hamsin da hudu (54).” Yace.

Kwamishinan ‘yan sandan ya ce rundunar ta aiwatar da sabbin dabarun tunkarar kalubalen tsaro da suka kunno kai, da inganta hadin gwiwar al’umma, da inganta jin dadin jama’a da horar da jami’ai da maza.

Ya bukaci mazauna yankin da su marawa rundunar ‘yan sandan Najeriya da sauran jami’an tsaro goyon baya a kokarinsu na ganin jihar Jigawa da Najeriya ta samu zaman lafiya.

legit breaking news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp