Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta kama wasu mutane 1,254 da ake zargi da aikata laifuka da suka hada da garkuwa da mutane, fashi da makami, sata, barna da sauransu.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar CP. AT. Abdullahi ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai nasarorin da rundunar ta samu a shekarar 2024.
A cewarsa, an kama mutane 1,254 bisa manyan laifuka daga ranar 20 ga Nuwamba, 2023 zuwa yau.
“Mutane tamanin da takwas (88) da ake zargi da yin fashi da makami, da masu garkuwa da mutane goma sha tara (19), wadanda ake zargi da aikata laifin fyade dari da ashirin (120) da kuma dari da hamsin da takwas (158) da ake zargin sun aikata laifin kisan kai.
“Sauran sun hada da, mutane dari takwas da sittin da tara (869) da ake zargi da aikata wasu laifuka kamar: Barna, Satar Shanu, Satar Dabbobi, Satar Muggan Kwayoyi, Satar Babura, Satar Motoci da Zamba.
“An kwato bindigogi goma sha bakwai (17), da suka hada da guda uku (3) AK-47, Bidistol daya (1), Bindigogin Dane guda goma (10), bindigu na gida guda uku (3) da kuma harsasai guda hamsin da hudu (54).” Yace.
Kwamishinan ‘yan sandan ya ce rundunar ta aiwatar da sabbin dabarun tunkarar kalubalen tsaro da suka kunno kai, da inganta hadin gwiwar al’umma, da inganta jin dadin jama’a da horar da jami’ai da maza.
Ya bukaci mazauna yankin da su marawa rundunar ‘yan sandan Najeriya da sauran jami’an tsaro goyon baya a kokarinsu na ganin jihar Jigawa da Najeriya ta samu zaman lafiya.