fidelitybank

Ƴanbindiga sun kashe Jami’an sa kai 15 a Katsina

Date:

Rundunar ƴansandan jihar Katsina ta tabbatar da kai wani hari kan wasu jami’an ƙungiyar tsaro ta Community Watch Corps a jihar, wanda ya yi sanadin mutuwar aƙalla mutum 25.

Lamarin ya faru ne ranar Laraba lokacin da jami’an tsaron na Community Watch Corps, suka yi zango a garin Ɓaure na jihar ta Katsina, bayan ziyarar ta’aziyar ɗaya daga cikin abokin aikinsu da ya mutu sakamakon harin ’yanbindigar.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shida lamarin ya shaida wa BBC cewa kwantan ɓunar-da ‘yanbindigar suka yi wa jami’an ya janyo mutuwar fiye jami’an na Community Watch Corps 10.

‘’Bayan sun tsaya ne, sai kwatsam ‘yanbindigar suka buɗe musu wuta, kuma sun kashe aƙalla mutum 15’’, in ji shi.

Ya kuma ce bayan kashe mutanen ‘yanbidigar sun hana a ɗauki gawarwakinsu har sai ranar Alhamis da safe.

Bayan kashe jami’an tsaron na ‘Community Watch Corps’, mutanen gari sun fantsama kasancewar ranar kasuwar gari ne, lamarin da ya sa aka kashe wasu daga cikinsu, inda har yanzu ba a ga wasu mutanen ba kamar yadda wasu mazauna yankin suka bayyana wa BBC.

‘’Sun kashe mutanen ƙauyukan yankin masu yawa, aƙalla mutanen da suka kashe sun kai mutum 25’’, a cewar wani da ya shaida lamarin.

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar Katsina,Abubakar Sadiq Aliyu ya tabbatar wa BBC faruwar lamarin, sai dai ya ce suka ci gaba da tattara bayanai.

Yankunan ƙananan hukmomin Safana da Batsari na daga cikin yankunan jihar Katsina masu mafa da matsalar tsaro.

sspdf news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp