Tsohon shugaban jam’iyyar All Progressive Grand Alliance, APGA na kasa, Sanata Victor Umeh, ya koka kan yawan ‘yan takarar shugaban kasa daga shiyyar Kudu maso Yamma, ya kuma zarge su da rashin aikin samar da zaman lafiya da hadin kan Nijeriya.
A cewar Umeh, bayan Cif Olusegun Obasanjo ya yi shekara takwas a matsayin shugaban kasa, sannan kuma Farfesa Yemi Osinbanjo zai yi shekara takwas a matsayin mataimakin shugaban kasa, shiyyar Kudu maso Yamma ba ta da wata hujjar da za ta iya tsayawa takarar shugaban kasa a 2023.
Umeh ya ce, matakin da suka dauka ya hada da aiki don wargaza Najeriya, saboda ba su da ruhin karbar wasu.
Ya ce, “A yankin Kudu maso Yamma, za ka ga da yawa daga cikin masu neman shugabancin kasar nan suna shelanta. Yana da ban dariya. Kudu maso yamma ne suka samar da Obasanjo na tsawon shekaru takwas, kuma dansu shine mataimakin shugaban kasa a yanzu kuma za su yi shekara takwas a shekara mai zuwa, kuma zabe na gabatowa kuma dukkansu suna bayyanawa.
“Ina tsammanin suna neman wargajewar Najeriya ne. Domin idan har suna son Nijeriya ta zama dunkulalliyar kasa, ba za su nemi su mamaye wannan ofishin ba a 2023. A bar su a hada kansu waje guda a kan manufa daya na samun kasa mai dabi’a.