Tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Jonathan, ya bukaci ‘yan takara da kuma sauran ‘yan siyasa a kan su rika taka-tsantsan a kan dorewar kasa da kuma sanya jin dadi da walwalar al’ummar kasar a gaba a yayin yaki neman zabe.
Goodluck Jonathan, ya yi wannan kira ne a ranar Alhamis a wajen taron shekara-shekara kan irin tariin da tsohon shugaban mulkin sojan kasar Ibrahim Badamasi Babangida ya kafa.
A cewarsa, yana da matukar muhimmanci ga ‘yan Najeriya su kawar da dukkan wasu bambance-bambancen da ke tsakaninsu, su shiga a dama da su a cikin harkokin siyasa don zabar shugabannin da za su kawo sauyi a kasar.
Ya ce,” Zabuka masu zuwa suna da matukar muhimmanci wajen ci gaban mu, a don haka ne nake jan hankalin ‘yan siyasa da su rinka taka-tsantsan wajen hada kai da kuma samar da zaman lafiya a kasa.”
Jonathan, ya ce a wannan lokaci da ake ciki bai kamata mu rinka nuna halin ko in kula da abubuwa da suka dace mu mayar da hankali a kai ba, dole mu sanya a ran mu cewa zamu shiga a dama damu a cikin harkokin siyasa.Dole kuma mu wayar wa da sauran ‘yan uwanmu kai a kan muhimmancin kada kuri’a a lokacin zabe.