fidelitybank

Ƴan Sandan sun kashe riƙaƙƙen ɗan bindiga a Katsina

Date:

Rundunar ƴan sandan jihar Katsina, ta ce, ta daƙile wani hari da aka kai Magamar Jibiya da Ƙaramar Hukumar Jibiya duk a Jihar Katsina tare da kashe wani gawurtaccen ɗan bindiga.

A wata sanarwa da mai magana da yawun ƴan sanda jihar SP Gambo Isah ya fitar, ƴan sandan sun ƙwace bindiga ƙirar AK 47 guda ɗaya da ƙundun harsasai guda huɗu da ke ɗauke da harsasai 90.

Ɗan bindigan da aka kashe sunansa Ibrahim Dangawo wanda ake zargin shi ya kitsa wani hari da aka kai har aka kashe wani tsohon DPO na Jibiya wato DSP Abdulkadir Rano.

A jiya Litinin da misalin huɗu da rabi na yamma ne ƴan bindiga suka rinƙa harbi kan mai uwa da wabi inda suka kai hari kan wani shingen binciken ƴan sanda a Magama a kwanar Hirji a kan hanyar Jibiya.

Bayan musayar wuta da ƴan sandan suka yi da su, a nan ne ƴan sandan suka daƙile harin tare da ƙwace wasu makamansu.

Sanarwar ta ce akasarin yan bindigan da suka tsira daga harin sun tsira da raunin harbin bindiga.

today nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...

Ambaliyar ruwa ta kashe mutuane takwas a Ebonyi

Ambaliya, wadda mamakon ruwan sama ya janyo, ta yi...

Bankin Duniya zai kashe wa yankin Arewa a Najeriya dala miliyan 300

Bankin Duniya ya amince da kasafin kuɗi dala miliyan...

Giyar mulki na kwasar Trump – ‘Yan Majalisar Democrat

'Yan Democrats a Amurka sun zargi Donald Trump da...

Kama Aminu Waziri Tambuwal da EFCC ta yi ba daidai ba ne – PDP

Jam'iyyar PDP a jihar Sokoto ta yi Allah-wadai da...

An kai hari a ƙauyuka 15 na Zamfara a mako ɗaya – Rahoto

Wani rahoto da tashar Channels ta ruwaito daga cibiyar Zamfara Circle...

Jihohin Arewa huɗu ne suke biyan mafi ƙarancin fansho na N32,000 – NUP

Ƙungiyar ƴan fansho na arewacin Najeriya, NUP ta ce...
X whatsapp