fidelitybank

Ƴan Sandan na neman mai tsokanar mutane a TikTok ruwa a jallo

Date:

Rundunar ƴan sanda, sun yi kira ga duk wanda ya san wani mai shirya bidiyon tsokana a intanet ya ɓatawa, su fito su kai rahoto a kan irin halin da suka shiga.

Trinity Guy yana yin bidiyo ta hanyar shirya labari a kan tsokanar mutane don wallafawa a shafukan sada zumunta kuma dubban mutane ne suke bibiyar harkokinsa.

Wasu daga cikin bidiyon da yake shiryawa sukan nuna shi a lokacin da yake roƙon afuwa da magiyar kada a halaka shi, kafin a ji ƙarar tashin wani abu mai kama da bindiga, daidai lokacin da shi kuma zai faɗi magashiyan tamkar wanda aka harbe.

Irin wannan bidiyo dai na tayar da hankalin mutanen da ke kusa, inda sukan yi matuƙar kaɗuwa, wasu ma su ruga da gudu cikin firgici.

“Ina ganin ya kamata a kama mutumin. Ya kamata mutanen da kan shiga fargaba ta dalilin bidiyon Trinity Guy su rika kai rahoton masu irin wannan wasan barkwanci saboda yawancin ayyukansu na da alaƙa da aikata laifi da fasikanci, da kuma mugunta,” in ji kakakin rundunar ‘yan sanda ta Najeriya, Olumuyiwa Adejobi.

Ya kara da cewa “Wadannan matan na da hujjar yin shari’a sosai a kan mai bidiyon tsokanar.”

Wasu a shafukan intanet sun mayarwa ‘yan sanda martani, suna cewa kamata ya yi rundunar ta yi maganin cin zarafi da rashawar da ta janyo zanga-zangar EndSars ta Najeriya, maimakon ɓugewa da yunƙurin kama masu shirya bidiyon barkwanci don tsokana.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp