Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya yi kira ga ƴan Najeriya su ƙara haƙuri da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu duk da yanayin da ƙasar ke ciki na wahalar rayuwa.
Ganduje ya bayyana haka ne a saƙonsa na Kirsimeti da sakataren watsa labaransa, Edwin Olofu, ya fitar, inda ya ce ƴan Najeriya za su dara domin tattalin arzikin ƙasar zai inganta a 2025, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
Ganduje ya ce, “Ƴan Najeriya su ƙara haƙuri da gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu musamman game da matakan da ya ɗauka na inganta tattalin arziki waɗanda suka jawo wa ƴan ƙasar rashin jin daɗi.
“Tuni an fara ganin sakamakon gyare-gyaren. Zuwa bikin Kirsimetin baɗi, tattalin arzikin ƙasar ya gyaru. Ɓangaren tsaro ma an fara ganin sakamako mai kyau domin an rage harkokin ƴanbindiga.”