fidelitybank

Ƴan Najeriya ku sake baiwa APC dama a 2023 – Shugaban Majalisa

Date:

Shugaban majalisar dattawa, Dr Ahmad Ibrahim Lawan, a karshen mako a Ilorin, babban birnin jihar Kwara, ya roki ‘yan Najeriya da su baiwa jam’iyyar APC mai mulki damar sake mulkin kasar nan har zuwa 2023.

Ya yi wannan roko ne a wani taro na gari da Sanata mai wakiltar Kwara ta tsakiya a majalisar dattawan kasar, Dakta Ibrahim Yahaya Oloriegbe ya kira a dakin taro na Banquet Hall daura da gidan gwamnati a Ilorin.

Oloriegbe ya kuma yi amfani da wannan dama wajen bayyana aniyarsa ta sake tsayawa takara a karo na biyu.

Tun da farko dai shugaban majalisar dattawan ya kaddamar da ginin wata cibiyar gyara ma’aikatan jinya da ke asibitin kula da masu tabin hankali na tarayya da ke Budo-Egba a karamar hukumar Asa, tare da kaddamar da cibiyar Idi-Isin Community Heatlh Centre da ke Unguwar Okolowo a Ilorin, wanda Oloriegbe ya taimaka.

Lawan, ya ce, jam’iyyar APC mai mulki ta cika alkawuran da ta yi wa ‘yan Najeriya, dalilin da ya sa ya ce, kamata ya yi a sake baiwa jam’iyyar damar ci gaba da rike madafun iko a dukkan matakan mulki fiye da 2023.

legit breaking news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp