Wasu ‘yan bindiga da ake zargin ‘yan ta’addar Boko Haram/ISWAP ne, sun kashe manoma akalla hudu a yankin Kerawa da ke kan iyaka a karamar hukumar Gwoza ta jihar Borno.
An ce lamarin ya faru ne a ranar Alhamis tsakanin karfe 12 zuwa 1 na rana a yayin da manoman ke aikin gonakinsu.
Wannan na zuwa ne kawai watanni biyu bayan da wasu bama-bamai suka hallaka sama da mutane 30 a garin Gwoza.
Mai ba da shawara na gundumar Jimini, Bukar Aji da shugaban kungiyar al’ummar Kerawa Yakubu Ali, sun tabbatar da faruwar lamarin.
Jaridar DAILY POST ta bayar da rahoton cewa, garin Kerawa na kan iyaka da kasar Kamaru a tsaunin Mandara, inda aka san ‘yan ta’addan na buya.
A halin da ake ciki, jami’in ‘yan sanda na shiyya ta Gwoza ya ce bai san da faruwar lamarin ba, inda ya yi alkawarin tabbatar da rahoton.
DPO ya ce harin na iya kasancewa daga Kerawa ne na kasar Kamaru, ba wai Kerawa na Najeriya ba, ya kara da cewa an yi irin wannan kisan a wasu makonni baya a garin Kerawa na kasar Kamaru, amma jama’a sun rikitar da yankin Kerawa na Najeriya.
DAILY POST ta tuna cewa an taba ayyana Gwoza a matsayin halifancin ‘yan ta’adda a lokacin da aka kama ta a shekarar 2014, kafin daga bisani dakarun sojojin Najeriya su kwato su.