Akalla mutane 14 ne aka yi garkuwa da su a lokacin da wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne suka kai hari a wani masallaci da ke karamar hukumar Giwa a jihar Kaduna.
Rahotonni sun ce, daya daga cikin masu ibadar, Alhaji Buhari Nadama, wanda ya ce da kyar ya tsere, ya bayyana cewa, sun ji karar harbe-harbe a lokacin da suke sallar magariba.
Ya ce, bayan mintuna kadan, sai suka ga wasu mutane da suka rufe fuska, wadanda ke dauke da makamai.
A cewarsa, ‘yan bindigar sun kuma tafi da wasu shanu daga wata unguwar da ke kusa da su, Tudun Amada.
Har ila yau, wani shugaban al’ummar yankin, Alhaji Dauda Mustapha ya bayyana cewa, yayin da wasu ‘yan ta’addan ke gudanar da ayyukansu a cikin masallacin, wasu kuma sun binciki gidaje da dama, inda suka dauko mata.
Sai dai wani mazaunin garin ya shaidawa kafar yada labarai cewa, an sako hudu daga cikin wadanda aka sace a daren Juma’a.
A halin yanzu, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan Kaduna, ASP Mohammed Jalige bai tabbatar da faruwar lamarin ba.