Jama’a sun tsere daga gidajensu a kauyukan karamar hukumar Wase ta jihar Filato, sakamakon yawan hare-haren da ‘yan bindiga ke kaiwa yankin.
Maharan sun farmaki kauyen Anguwan Ali inda suka bude wuta kan al’umma, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane da yawa.
Hakazalika a na zaman dar-dar a garin Bunyun, sakamakon hare-haren ƴan bindigar.
Daily Trust ta rawaito cewa, mazauna kauyuka a karamar hukumar Wase ta jihar Filato sun tsere daga gidajensu, yayin da ‘yan bindiga suka tsananta kai hare-hare a yankunan.