Wasu ‘yan bindiga sun kai hari a garin Dutsin-Ma da ke jihar Katsina a daren ranar Talata, inda suka yi awon gaba da dalibai biyu na Jami’ar Tarayya ta Dutsin-ma da ke unguwar Gidan Rediyon Bayan Gidan.
Wani mai sharhi kan harkokin tsaro, Bakatsine ne ya bayyana lamarin a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X ranar Laraba.
A cewar Bakatsine, mahara dauke da makamai sun far wa yankin da daddare, lamarin da ya haifar da firgici a tsakanin mazauna yankin kafin su yi awon gaba da daliban.
“A daren jiya ‘yan bindiga sun kai hari garin Dutsin-Ma a jihar Katsina, inda suka yi awon gaba da dalibai biyu na Jami’ar Tarayya Dutsin-ma da ke unguwar Bayan Gidan Rediyo.”
Kokarin jin ta bakin rundunar ‘yan sandan jihar domin jin ta bakinsa ya ci tura har zuwa lokacin da ake hada wannan rahoto.