fidelitybank

Ƴan Bindiga sun sace Hakimi da tawagarsa a Kaduna

Date:

Kungiyar Kudancin Kaduna (SOKAPU) ta yi Allah wadai da sace Hakimin Garu Kurama da wasu ’yan kabilar Gurzan Kurama guda shida a karamar hukumar Kauru ta Jihar Kaduna a daren Juma’a.

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na kungiyar, Josiah Yusuf Abraks ya fitar, ya bayyana sunayen wadanda aka sacen da suka hada da Yakubu Jadi (Hakimin gundumar), Iliya Yakubu, Nehemiah Tanko, Thomas Tanko, diyar Yakubu Jadi da kuma Cocin Katolika na al’ummar yankin.

SOKAPU ta bayyana lamarin a matsayin abin takaici, abin tsoro da damuwa.

A cewar sanarwar, “SOKAPU tana kira ga hukumomin tsaro da hukumomin da abin ya shafa da su yi iya kokarinsu don ganin an sako hakimin gundumar Mista Yakubu Jadi da sauran mutane biyar cikin gaggawa.”

Kungiyar ta kuma yi kira ga gwamnati a dukkan matakai da su kara kaimi wajen kare rayuka da dukiyoyi.

Hakazalika kungiyar ta yi kira ga al’umma da su kara taka tsan-tsan tare da lura da yadda ba a saba gani ba, da kuma motsin da ba a saba gani ba a yankunansu, inda ta shawarce su da su kai rahoto ga hukumomin da suka dace.

the sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp