Rahotanni daga ƙaramar hukumar mulkin Shiroro a jihar Neja na cewa, wasu da ake zargin mayaƙan kungiyar Boko Haram ne sun kashe sama da mutum goma sha biyu tare da ƙona kimanin gidaje talatin a wasu jerin hare-hare da suka kai.
Mazauna yankunan sun ce hare-haren sun faru ne a tsawon makon da ya gabata, a garuruwan Alawa da Bangajiya da sauran su, inda baya ga kashe mutane da dama da maharan suka yi sun kuma yi awon gaba da dukiya mai ɗimbin yawa.
Wani Mazaunin garin ya shaida wa BBC cewar sama da makonni biyu ke nan suke fama da tashe tashen hankula na hare-haren ƴan bindiga waɗanda suka hana su sukuni.
A cewar sa, a makon da ya gabata ne ƴan bindigar suka dasa bam a hanya wanda ya tashi da wasu da ke kan hanyar komawa ƙauyukansu daga kasuwa kuma nan take mutane aƙalla takwas suka rasa rayukansu.
Da aka je kwashe gawawwakin waɗanda aka kashe kuma aka sake kai wani harin da ya yi sanadiyar asarar rayuka sannan suka hana daukar gawawwakin wanda har ya zuwa yanzu babu labarin kwashe gawawwakin.
Shugaban ƙaramar Hukumar Shiroro Hon. Akiku Kuta ya tabbatar da harin
Wadannan sabbin hare-haren dai sun sa mutane da dama yin hijira zuwa wasu makwabtan garuruwa