fidelitybank

Ƴan bindiga sun kashe mutane tare da yin garkuwa da wasu a Zamfara

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kashe mutane da dama tare da yin garkuwa da wasu a kauyen Gada da ke karamar hukumar Bungudu a jihar Zamfara.

Wani dan kauyen mai suna Ibrahim Musa ya bayyana haka a wata hira da manema labarai ta wayar tarho cewa yan ta’addan sun kai farmaki kauyen ne da misalin karfe 6 na yammacin ranar Asabar.

“’Yan bindigar dauke da manyan muggan makamai, sun iso kan babura da yawa kuma suka fara harbi ba kakkautawa kan mutanen kauyen. Mun yi asarar mutane bakwai a wannan danyen aikin, inda aka yi garkuwa da mutane da dama,” ya kara da cewa.

Rahotanni na cewa harin ya faru ne kwana guda bayan da gwamnan ya tafi jihar Imo domin jagorantar tawagar jam’iyyar PDP a zaben gwamna.

Musa ya bukaci gwamnatin tarayya da ta sa baki wajen ceto al’ummar jihar Zamfara, ganin yadda lamarin ke kara ta’azzara.

“Babu wanda yake cikin koshin lafiya a jihar, kuma muna rokon gwamnatin tarayya da ta kara tura jami’an tsaro a jihar Zamfara domin dakile ayyukan ‘yan bindigar da suka addabi jihar.”

Kokarin da manema labarai suka yi a Gusau babban birnin jihar domin jin ta bakin kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Yazid Abubakar, ya ci tura har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

nnn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp