fidelitybank

Ƴan bindiga sun kashe mutane 7 a Zamfara

Date:

Kimanin sa’o’i 24 da ‘yan bindiga suka kashe mutane 56 a kauyuka uku da ke karamar hukumar Bakura ta jihar Zamfara, wasu ‘yan bindiga sun sake kashe wasu mutane bakwai a karamar hukumar Maradun ta jihar.

Kananan hukumomin Maradun da Bakura sun raba kan iyaka.

A sabon harin da aka kai da yammacin ranar Asabar, wata majiya a Maradun ta ce, an kai hari kauyuka biyu Faru da Kauyen Minane.

“Ina babban asibitin Maradun lokacin da sojoji suka kawo gawarwakin wadanda aka kashe,” in ji Jamilu Muhammad.

“Mutanen mu da ke kauyen Garin Minane sun ce ‘yan bindigar sun kai farmaki garin ne da misalin karfe 2 na rana inda suka fara harbe-harbe kai tsaye. Abin da suka saba yi shi ne gida-gida don neman dabbobin gida ko wasu kayayyaki masu daraja amma a jiya da suka shiga kauyen sai suka fara harbe-harbe ba da dadewa ba,” inji shi.

A cewarsa, an kashe mutane shida a Garin Minane yayin da aka kashe daya a Faru. Ya ce adadin wadanda aka kashe na iya karuwa saboda da yawa sun bace a kauyukan da lamarin ya shafa.

vanguard (nigeria)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp