fidelitybank

Ƴan bindiga sun harbe Soja tare da jikkata wasu a Kaduna

Date:

Wasu ‘yan bindiga a ranar Talata da yamma, sun harbe wani soja har lahira yayin da wasu uku suka samu raunuka, yayin musayar wuta a kauyen Akoti da ke kusa da garin Kagarko a jihar Kaduna.

Wani mazaunin unguwar mai suna Musa Arungo, wanda ya tabbatar wa da manema labarai faruwar lamarin, ya ce wani farar hula kuma ya samu rauni yayin artabun da ‘yan bindigar suka yi.

A cewarsa, lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata.

Ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi awon gaba da shanu sama da 80 kuma suna wucewa ta kauyen Akpoti ne aka sanar da sojoji.

“Abin takaici, ‘yan bindigar sun kashe soja daya, suka raunata uku a yayin da ake aikin.

“Daya daga cikin mutanen kauyen ya samu harsashin bindigar da ‘yan bindigar suka yi masa, kuma a halin yanzu yana jinya a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abuja (UATH) da ke Gwagwalada,” inji shi.

Shi ma Madaki na Janjala, Samaila Babangida, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya kara da cewa “daga bayanan da na samu a safiyar yau, sojoji sun fito daga Kaduna domin kwashe sojoji uku da suka jikkata da kuma gawar wanda aka kashe.”

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, DSP Mohammed Jalige, bai amsa kiran waya da sakonnin tes da aka aika masa ba.

daily post nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp