fidelitybank

Ƴan bindiga sun harbe jami’in INEC a Imo

Date:

 

An harbe Nwokorie Anthony, jami’in Hukumar Zabe mai Zaman Kanta ta Ƙasa, INEC a Jihar Imo.

An kashe jami’in ne a yayin da ake ci gaba da gudanar da aikin rijistar zaɓe (CVR) a Ƙaramar Hukumar Ihitte Uboma da ke jihar.

A cewar Kwamishinan Zabe na jihar, Resident, Farfesa Emeka Ezeonu, an kashe Nwokorie ne a Nkwo Ihitte (mazaɓar 004) da ke mazaɓar Amakohia (RA 02) na Ƙaramar Hukumar Ihitte Uboma, sannan ba a san inda wasu ma’aikatan biyu da ke aikin rajistar su ke ba. .

A bisa wannan mumunan lamarin, hukumar zaɓen ta dakatar da gudanar da aikin rijistar katin zaɓen a karamar hukumar.

Kwamishinan INEC na kasa kuma shugaban kwamitin yada labarai da wayar da kan masu kaɗa kuri’a, Festus Okoye ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis.

Kafin faruwar wannan lamari, hukumar ta dakatar da CVR a Ƙananan Hukumomin Osu da Njaba na jihar saboda rashin tsaro, yayin da ake gudanar da aikin a ofishin INEC na Ƙaramar Hukumar Oru Gabas, Oru ta Yamma, Orlu da Ohaji-Egbema.”

“Hukumar na mika ta’aziyyarta ga iyalan Nwokorie Anthony tare da addu’ar Allah ya basu ikon jure rashin. An kai rahoton faruwar lamarin ga jami’an tsaro domin bankado al’amuran da suka haifar da wannan mummunan lamari tare da gurfanar da masu laifin a gaban kuliya,” inji Okoye.

www.najnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...
X whatsapp