fidelitybank

Ƴan Bindiga sun hallaka DPO bayan sun kai hari jihar Delta

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane sun kai hari tare da kashe wani DPO na ƴansanda a karamar hukumar Ughelli ta Arewa da ke jihar Delta.

Mai magana da yawun ƴansandan jihar, Bright Edafe, shi ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Litinin, inda ya ce ƴan bindigar sun kuma raunata wani DPO na shiyyar Ororoekpe inda aka garzaya da shi asibiti domin ba shi kulawa.

Edafe ya ce jami’an ƴansandan biyu sun fita samame ne da wasu jami’ai lokacin da ƴan bindigar suka yi musu kwantan-ɓauna, inda ya ce ana ci gaba da bin tsawunsu da nufin kama su.

Kakakin ƴansandan ya kuma ruwaito karya doka da oda a wata karamar hukumar Aniocha ta Arewa na jihar inda matasa suka far wa kayayyaki tare da cinna musu wuta.

A cewarsa, tarzomar ta ɓarke ne bayan lakaɗawa wani mutum duka har ta kai ga mutuwarsa da wani yayi wanda suke zargi da kwace filayen al’umma a yankin.

Wasu jagororin al’umma sun nuna adawa da matakin abin da ya janyo tarzomar da ta yi sanadiyyar ran mutumin.

Edafe ya bayyana cewa an kama mutum uku da ake zargi da aikata laifin kuma ana ci gaba da bincike.

naija legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp