fidelitybank

Ƴan bindiga sun fara ofishin ƴan sanda a Zamfara

Date:

Akalla mutane bakwai ne ake fargabar sun mutu a wani hari da wasu ‘yan bindiga dauke da makamai suka kai a shalkwatar rundunar ‘yan sanda da ke garin Zurmi, a karamar hukumar Zurmi a jihar Zamfara.

Rahotanni na cewa ‘yan bindigar sun kai wa Zurmi hari da yammacin ranar Lahadi, inda suka kashe mutane bakwai ciki har da dan sanda guda.

Babangida Zurmi, dan asalin garin, ya shaida wa manema labarai cewa har yanzu bai yi magana da wani dan uwansa ba har zuwa karfe 9:45 na dare.

“Yayin da muke magana yanzu, ba zan iya tuntuɓar kowa a garin ba, lambobin su a kashe suke. Hakan na nufin har yanzu ‘yan fashin na nan a wajen. Muna bukatar taimako daga hukumomin da abin ya shafa,” inji Zumi.

Wata majiya daga yankin ta ce, ‘yan bindigar sun kai hari garin ne da nufin daukar fansa kan kisan da ‘yan banga suka yi wa mutane biyu a yankin.

A cewarsa, an kona shaguna da dama sannan an kuma kona hedikwatar ‘yan sanda da ke Zurmi.

A wani labarin kuma, wasu gungun ‘yan bindiga da ke aiki a karamar hukumar Maradun sun kashe mutane hudu tare da yin awon gaba da wasu da dama.

A cewar majiyoyi, mutane hudun sun mutu ne a lokacin da ‘yan bindigar suka bude wuta kan mutanen da ke share ciyayi a kan hanyar.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara, Yazid Abubakar, ya tabbatar da faruwar harin, inda ya ce yana ci gaba da tattara bayanai kan harin na Zurmi.

www.legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp