fidelitybank

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Date:

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar hukumar Dan Musa ta jihar Katsina sun ajiye makamansu tare da sakin mutum 16 da suka yi garkuwa da su.

Cikin wata sanarwa da rundunar sojin Najeriya ta wallafa a shafinta na X, ta ce matakin na cikin wani shiri na ci gaba da karɓar makamai da ficewa daga harkar aikata laifuka wanda rundunar Operation Fasan Yamma ke jagoranta tare da hadin gwiwar hukumomi da sauran masu ruwa da tsaki.

Jagororin ‘yan bindigar da suka miƙa wuya sun haɗa da Kamulu Buzaru da Manore da Nagwaggo da Lalbi da Alhaji Sani da Dogo Baidu da Dogo Nahalle da Abdulkadir Black.

A cewar jami’an tsaron, fitattun ƴanbindigar sun miƙa makamansu ne a ranar 14 ga Yuni, 2025, tare da yin alƙawarin barin aikata laifi da zama lafiya da sauran al’ummomi.

An karɓi makamansu kuma an adana su a karkashin kulawar hukumomi, kamar yadda jami’an tsaron suka tabbatar.

Domin tabbatar da zaman lafiyar, tsoffin ‘yan bindigar sun saki mutum 16 da suka haɗa da mata bakwai da yara tara da suke tsare da su, tare da alƙawarta sakin wasu da dama.

Hukumomin soja sun bayyana cewa bayan wannan mataki, lamarin tsaro a yankin Dan Musa ya daidaita, tare da ci gaba da sanya ido daga dakarun soji don hana sake faruwar rikice-rikice.

naija news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...
X whatsapp