fidelitybank

Ƙungiyoyi sun allawadai da kama matashi da gwamnatin jihar Sokoto ta yi

Date:

Gamayyar Kungiyoyin Kare Haƙƙin ɗan Adam da na Matasa a Jihar Sokoto sun koka da kama wani matashi a jihar.

Ƙungiyoyin sun bayyana koken ne a cikin wata takarda da suka fitar, inda suka yi Allahwadai da tsare matashin mai Shafiu Umar Tureta, mataimaki na musamman kan harkokin yaɗa labarai ga tsohon gwamnanar jihar, Sanata Aminu Waziri Tambuwal da ake zargin gwamnatin Jihar ta sa aka yi da kuma gurfanar da shi gaban kotu.

Ƙungiyoyin sun ce tsare Tureta cin zarafi ne ga ƴancin ɗan adam.

A cewar takardar koken, ƴan sanda sun kama Tureta bisa umarnin gwamnatin jihar bayan ya yaɗa wasu bidiyoyi a shafin sada zumunta na Facebook wanda ke nuna Gwamnan Jihar Aliyu na ƙoƙarin yin magana da Ingilishi da kuma wani wanda ya nuna shi yana liƙa dalar Amurka a wajen bikin zagayowar ranar haihuwar uwargidan gwamnan.

Lamarin da ya janyo suka daga ɓangarori da dama bisa la’akari da irin halin matsi da ake ciki a Najeriya.

Ƙungiyoyin sun bayyana cewa yayin da matar gwamnan da sauran waɗanda suke liƙin a cikin bidiyon ba su fuskanci wani hukunci na shari’a ba, bai kamata a hukunta Tureta ba kan wallafa bidiyon. In ji BBC.

Takardar ta jaddada cewa kamun Tureta ya saɓa wa ‘yancin faɗin albarkacin baki da tsarin mulki ya tanadar.

Ƙungiyoyin sun kuma yi kira ga Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) da ta shiga tsakani, inda ta buƙace ta da ta shawarci gwamnatin Jihar Sokoto da ɓangaren shari’a da su kaucewa wa ayyukan da za a iya ɗauka a matsayin cin zarafi na ‘yan kasa.

Sun kuma buƙaci a gaggauta sakin Tureta ba tare da wani sharaɗi ba.

thisday newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp