fidelitybank

Ƙungiyar Ƙwadago ta fara yajin aikin sai baba ta gani

Date:

Manyan ƙungiyoyin ƙwadago a Najeriya, NLC da TUC sun buƙaci mambobinsu da su daina aiki daga ranar Talata, yayin da suke shiga yajin aikin na sai-baba-ta-gani a fadin ƙasar duk kuwa da umarnin da kotu ta bayar na hana su yin hakan.

Ƙungiyoyin dai na matsa wa shugaban ƙasar Bola Tinubu ne ya dawo da tallafin man fetur din da aka kwashe shekaru ana amfani da shi a baya, wanda ke sanya farashin man fetur yin rahusa.

Amma gwamnatin ta ce tana la’akari da tabarbarewar tattalin arziƙin ƙasar, tare da shirin karkatar da kudadenta wajen gudanar da ayyukan jin kai.

Ƙungiyoyin dai na son gwamnati ta ƙara mafi karancin albashin ma’aikata zuwa akalla dalar Amurka 120 daga kusan dala 36, tare da sauya wasu manufofinta na tattalin arziki da ba su yi wa talakawa daɗi ba.

Shugaban TUC, Festus Osifo ya bayyana cewa yajin aikin zai ci gaba da tafiya har sai an samu kyakkyawan martani daga gwamnati a dukkan matakai.

Wannan matakin dai ya biyo bayan umarnin dakatar da yajin aikin da wata kotu da ke Abuja ta bayar a baya-bayan nan, koda yake har yanzu babu tabbas kan tsawon lokacin da yajin aikin zai gudana.

Amma ana sa ran zai shafi manyan ayyuka kamar asibitoci da tashoshin jirgin kasa, da makarantu a ƙasar mafi girman tattalin arzikin Afirka.

Kungiyoyin dai sun yi barazanar shiga yajin aikin akalla sau uku tun bayan da Tinubu ya hau kan karagar mulki a watan Mayu, amma sai aka yi gaggawar dakatar da su bayan ganawar da suka yi da shugaban, lamarin da ya sanya ayar tambaya kan yanke hukuncin nasu.

Ana kuma kallon yajin aikin na ranar Talata a matsayin nuna adawa da harin da aka kai wa shugaban ƙwadagon, Joe Ajaero a jihar Imo a makon da ya gabata.

nigeria newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp