fidelitybank

Ƙungiyar Ƙwadago ta baiwa Gwamnoni wa’adin mako biyu a biya albashin Naira 35,000

Date:

Ƙungiyar kwadago ta bai wa gwamnonin jihohi wa’adin mako biyu su fara tattaunawa kan batun biyan ƙarancin albashin Naira 35,000 ga ma’aikata a jihohinsu.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa wannan wa’adin ya yi daidai da sharuddan yarjejeniyar fahimtar juna da gwamnatin tarayya, da ƙungiyoyin kwadago ta Najeriya suka sanya wa hannu.

Sassan Jihohin ƙungiyoyin ƙwadagon sun ba da wa’adin makonni biyu inda suka tuntubi gwamnonin da su hanzarta aiwatar da shirin biyan ƙarancin albashin.

A wani labarin kuma, shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ƙaddamar da shirin bada tallafin kudi naira tiriliyan 1 da nufin taimakawa gidaje miliyan 15 domin rage raɗaɗin tattalin arzikin da ake samu na cire tallafin man fetur.

A ƙarkashin wannan shirin, kowane magidanci zai karbi Naira 25,000 na tsawon watanni uku, wanda ya kai kusan naira tiriliyan 1.13.

Ministar ma’aikatar jin ƙai, Dr. Betta Edu, ta bayyana cewa kimanin ‘yan Najeriya miliyan 61 ne za su ci gajiyar wannan tallafin kudi.

A baya dai shugabannin ƙungiyar ƙwadago sun cimma matsaya da gwamnatin tarayya a ranar 1 ga watan Oktoba, inda ta tanadi cewa duk ma’aikatan tarayya za su karbi ƙarancin albashin naira 35,000 daga watan Satumba, har sai an kammala sabon mafi karancin albashi na kasa.

assu update

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp