A yau Asabar ne Kungiyar Tarayyar Afirka AU za ta soma taronta na yini biyu, inda za a tattauna batutuwan da suka shafi yaƙi da kuma matsalar ƙarancin abinci.
Shugabannin ƙasashen AU za kuma su yi fatan ƙaddamar da yarjejeniyar cinikayya ba tare da shinge ba a nahiyar Afirka.
Ministoci daga Guinea da Burkina Faso da Mali za su halarci taron a Ethiopia duk da dakatar da su da aka yi sakamakon juyin mulkin da sojoji suka yi a kasashen inda suke neman a janye matakin.
Shugaban Comoros Azali Assoumani ne zai karɓi shugabancin kungiyar daga hannun Shugaban Senegal Macky Sall.