fidelitybank

Ƙungiyar Malamai ta NUT ta karrama Gwamnoni 6 harda na Kano

Date:

Ƙungiyar Malamai ta ƙasa NUT, ta kararrama wasu gwamnonin ƙasar nan shida kan abin da kira ‘ƙoƙarinsu bunƙasa harkokin ilimi a jihohinsu.

An gudanar da bikin karramawar ranar Asabar a Abuja, babban binrin ƙasar, lokacin da ƙungiyar ta gudanar da bikin ‘Ranar Malamai da Duniya’.

Gwamnonin da aka karrama a lokacin bikin sun haɗa da na Kano, Abba Kabir Yusuf, da na Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, da na Oyo, Seyi Makinde da na Benue, Hyacinth Alia da na Enugu, Peter Mbah da kuma gwamnan jihar Kebbi Nasir Idris.

Shugaban ƙungiyar NUT na ƙasa, Comrade Titus Ambe, ya ce an zaɓo gwamnonin ne la’akari da irin ƙoƙarinsu wajen bunƙasa fannin ilimi a jihohinsu, musamman tallafa wa malamai da samar da abubuwan ci gaba a fannin koyo da koyarwa a jihohinsu.

Cikin wata sanarwa da sakataren ya ɗa labaran gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, ya ce gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf – wanda ya yi jawabi a madadin sauran takwarorinsa gwamnonin shida, ya jaddada ƙudurin gwamnatinsa na ci gaba da bai wa fannin bunƙasa ilimi fifiko, saboda muhimmancinsa wajen ci gaban yara masu tasowa

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, wanda ya samu wakilcin sakataren gwamnan tarayya, Sanata George Akume ya yaba wa gwamnonin bisa jajircewarsu wajen bunƙasa fannin ilimi a jihohinsu.

legit.ng.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp