Ƙungiyar Malamai ta ƙasa NUT, ta kararrama wasu gwamnonin ƙasar nan shida kan abin da kira ‘ƙoƙarinsu bunƙasa harkokin ilimi a jihohinsu.
An gudanar da bikin karramawar ranar Asabar a Abuja, babban binrin ƙasar, lokacin da ƙungiyar ta gudanar da bikin ‘Ranar Malamai da Duniya’.
Gwamnonin da aka karrama a lokacin bikin sun haɗa da na Kano, Abba Kabir Yusuf, da na Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, da na Oyo, Seyi Makinde da na Benue, Hyacinth Alia da na Enugu, Peter Mbah da kuma gwamnan jihar Kebbi Nasir Idris.
Shugaban ƙungiyar NUT na ƙasa, Comrade Titus Ambe, ya ce an zaɓo gwamnonin ne la’akari da irin ƙoƙarinsu wajen bunƙasa fannin ilimi a jihohinsu, musamman tallafa wa malamai da samar da abubuwan ci gaba a fannin koyo da koyarwa a jihohinsu.
Cikin wata sanarwa da sakataren ya ɗa labaran gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, ya ce gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf – wanda ya yi jawabi a madadin sauran takwarorinsa gwamnonin shida, ya jaddada ƙudurin gwamnatinsa na ci gaba da bai wa fannin bunƙasa ilimi fifiko, saboda muhimmancinsa wajen ci gaban yara masu tasowa
Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, wanda ya samu wakilcin sakataren gwamnan tarayya, Sanata George Akume ya yaba wa gwamnonin bisa jajircewarsu wajen bunƙasa fannin ilimi a jihohinsu.