Ƙungiyar ECOWAS za ta gudanar da taron na musamman domin tattaunawa kan harajin kayayyaki da ƙungiyar ƙasashen AES suka lafta wa ƙasashenta.
Ƙasashen ECOWAS za su zauna ne a watan da ake ciki na Afrilu, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito daga jami’in watsa labarai na ƙungiyar ƙasashen Joel Ahofodji.
Ya ce, “za a yi taron ne a ranar 22 ga Afrilu kan harajin kashi 0.5 da ƙasashen AES suka lafta wa kayayyakin da ke shiga ƙasashensu da su daga ƙasashen ECOWAS.”
Da aka tambaye shi ko akwai yiwuwar ƙungiyar ECOWAS ɗin za ta mayar da martani wajen ɗora wa ƙasashen na AES haraji, sai ya ce, “a lokacin taron za a tattauna komai da komai.”
Ƙasashen AES wato Mali da Nijar da Burkina Faso da suke ƙarƙashin mulkin soji ne suka sanar da ɗora wa ƙasashen ƙungiyar ECOWAS da suka fice harajin kashi 0.5 kan kayayyakin da ake shiga da su, “domin samun kuɗaɗen shiga.”
Harajin zai fara aiki ne daga ranar 28 ga watan Maris, amma banda kayayyakin agaji.
Wannan ya saɓa da yadda aka saba na cinikayya da shiga da fitar da kayayyaki ba tare da shinge ba a tsakanin ƙasashen ECOWAS.