fidelitybank

Ƙasashe 58 sun amince Okonjo-Iweala ta yi tazarce a ƙungiyar WTO

Date:

Ƙasashe 58 daga cikin 164 mambobin Kungiyar Cinikayya ta Duniya (WTO) sun nuna goyon bayansu ga buƙatar neman shugabar ƙungiyar Ngozi Okonjo-Iweala ta yi tazarce wa’adi na biyu.

Ƙasashen sun bayyana goyon bayansu ne ga Okonjo-Iweala a babban taron ƙungiyar da aka gudanar ranar Litinin, kamar yadda WTO ke shirin tallafawa Intanet.

“Ƙungiyar Afirka da ake kira Africa Group ne ta gabatar da buƙatar cewa shugabar a shirye take ta yi wa’adi na biyu, kuma ta gabatar da buƙatar cewa a fara bin matakai na sake zaɓar ta ba tare da ɓata lokaci ba,” a cewar sanarwar.

Mambobin ƙungiyar 58 sun bayyana goyon bayansu ga Okonjo-Iweala a babban taron na WTO tare da yin kira ta fito ta bayyana aniyarta ta neman wa’adi na biyu.

Ƙasashen sun jinjina wa shugabar kan nasarorinta da kuma jajircewarta a wa’adinta na farko.

Okonjo-Iweala ta ce ta saurari buƙatar ƙasashen kuma za ta yi nazari game da buƙatar.

Okonjo-Iweala ƴar Najeriya, ita ce ta bakwai a matsayin shugabar WTO. Ta karɓi rantsuwar kama aiki ne a ranar 1 ga Maris a wa’adin farko na shekara huɗu kuma wa’adin zai ƙare ne a ranar 31 ga Agustan 2025.

Tsohuwar ministar kuɗi ta Najeriya ta kasance mace ta farko kuma ƴar Afirka da ta taɓa rike muƙamin shugabar Ƙungiyar Cinikayya ta Duniya. In ji BBC.

breaking news in nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp