Ƙungiyar ƙwadago ta TUC, ta yi gargaɗin cewa, matakin ƙarin kuɗin man fetur da NNPCL ta yi zai ƙara jefa ma’aikata cikin matsanancin talauci.
Cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, shugaban kungiyar ta TUC, Kwamared Festus Osifo, ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta janye matakin ƙarin kuɗin.
”Maimakon hakan gwamnati ta aiwatar da tsare-tsare da zai ƙarfafa kuɗin ƙasarmu, da kuma ɗaukar ƙwararan matakai domin sauƙaƙa wa ‘yan Najeriya raɗaɗin talaucin da suke ciki”, in ji sanarwar.
Kungiyar ta ce ya kamata a ɗauki irin wannan mataki ba tare da tuntuɓar masu ruwa da tsaki ba, inda ta bayyana hakan a matsayin rashin mutunta jin daɗin ‘yan Najeriya, musamman ma’aikata, waɗanda irin waɗannan manufofin suka fi shafa.
Osifo ya ƙara jaddada cewa “hauhawar farashin man fetur da wutar lantarki zai ƙara dagula ƙalubalen da ake fuskanta, wanda zai haifar da ƙarin wahalhalu da tashin hankali.”
“Ya kamata a ɗauki matakin gaggawa don maido da ƙwarin gwiwar jama’a da kuma hana ci gaba da taɓarɓarewar rayuwar ‘yan ƙasa,” inji shi.